Lafiya Jari Ce

  • Author: Vários
  • Narrator: Vários
  • Publisher: Podcast
  • Duration: 3:59:45
  • More information

Informações:

Synopsis

Shirin Lafiya yana tattaunawa da likitoci da mahukunta a game da kiyon lafiyar jamaa, Sanin sabbin magunguna da binciken kimiya ya samar. Ana gabatar da shirin a ranar Littinin da hantsi, tare da maimaici a ranar Talata da yamma.

Episodes

  • Sharhi kan ƙiba fiye da ƙima da ke baraza ga matasan Afirka

    26/05/2025 Duration: 10min

    Shirin 'Lafiya Jari Ce na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan hasashen da wata ƙungiya ta yi cewar nan da shekarar 2025 raɓin al'ummar Afirka masamman matasa za su fuskanci cutar ƙibar da ta wuce ƙima ko Obesity a turance.

  • Ƙaruwa masu kamuwa da cutar tarin fuka a sassan Jamhuriyar Nijar

    19/05/2025 Duration: 09min

    Shirin namu na wannan makon zai mayar da hankali ne kan ƙaruwar mutanen da ke kamauwa da cutar  babban tari, ko kuma tarin fuka, ko kuma TB a sassan Jamhuriyar Nijar, lamarin da ke zuwa a lokacin da ake fuskantar ƙarancin agajin magangunan yaƙi da wannan cuta. Wanmnan cuta na sahun daɗaɗɗun cutuka masu yaɗuwa, waɗanda wani kan iya goga wa wani.Abin da ya  sa ya zama wajibi a rika wayar da kan al'umma akan hanyoyin kariya daga ita.

  • Yadda aka sake samun ɓullar cutar Polio a Najeriya

    12/05/2025 Duration: 10min

    Shirin Lafiya jari ce a wannan makon ya yi duba na musamman game da dawowar cutar Polio a Najeriya, cutar da alamu ke nuna nasarar yaƙarta ke yiwa ƙasar kwan gaba kwan baya, lura da yadda a lokuta da dama ake sake ganin ɓullarta bayan nasarar kawar da ita, kodayake ƙwararru sun ce wadda ta ɓulla a wannan karon ba wadda aka saba gani ba ce kuma bata kai waɗanda suka gabace ta illa ba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu............

  • Annobar ƙyanda ta tilastawa mahukunta Nijar yin rigakafin ƙasa baki ɗaya

    05/05/2025 Duration: 10min

    Shirin Lafiya Jari ce na wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan shaushawar ƙyandar da mahukuntan Jamhuriyar Nijar suka jagoranta sakamakon ɓullar cutar wadda a duk lokacin da aka ga bazuwarta ta ke yiwa ƙananan yara illa matuƙa. Dai dai lokacin da duniya ta gudanar bikin makon rigakafi a ƙarshen watan Mayun da ya gabata, a Jamhuriyyar Nijar annobar ƙyanda ce ke ci gaba da yaɗuwa tare da galabaitar da ɗimbin ƙananan yara, lamarin da ya tilasta mahukunta ɗaukar matakan yiwa jama’a rigakafin wannan cuta mai haɗari.Cutar ta Ƙyanda ko Ado ko kuma Dusa na matsayin babbar matsalar kiwon lafiya ta yadda a duk lokacin da ta ɓulla ta kan haddasa asarar ɗimbin rayuka, kodayake a yanzu tuni ma’aikatar lafiya ta jagoranci aikin rigakafin na ƙasa baki ɗaya da zai shafi dukkanin ƙananan yara tun daga watanni 6 da haihuwa har zuwa shekarun 5 da nufin murƙushe cutar.Tsawon mako guda aka shafe daga ranar 18 zuwa 24 ga watan Mayu ana gudanar da rigakafin na ƙyanda a sassan Nijar wanda aka yiwa ƙananan y

page 2 from 2